Raliya page 9 na shafi'u dauda giwa
RALIYA
Littafin
Shafi"u dauda giwa
Typing:- sadeeq shehu shariff
Post:- Shuraih Usman
@shuraih 99%
Page 9
.
AYARIN 'yan sandan da suka kamo jarmai suka ci
birki a daidai ofishin A-C-P AMINU JANGWARZO"
tsayawarsu keda wuya suka fito da shi" nannade
da ankwa a hannayenshi tare da murgujejen
akwatin kudin" Dan sandan da yake dauke da
akwatin sun shashi a tsakiya rike da bindigogi"
domin kuwa suna fargavar wata kila yana da
layar bata"
.
.
Da shigarsu ofishin JANGWARXO suka sameshi
tare da A-C-P ßilya" 'yan sandan suka sara ma
tsofaffin sannan babban cikinsu yace-:
"An gama aiki yallabai gashi nan mun kamoshi a
motar haya xai gudu xuwa wani kauye" ga
akwatin da ya sato"
A-C-P JANGWARXO yayi saurin amshe akwatin a
hannunsu" sannan ya daka masu tsawa yace"
"ku daukeshi ku kaishi gidan tuhuma ku kulleshi"
kada a bari wani ya kusanci inda yake har xuwa
nan da lokacin da xan baku umarni nan gaba"
.
.
'yan sandan suka cakumi jarmai wanda bakinshi
ya karkace ya koma gepe daya" yana ta xubar da
jini" kamar gilmawar walkiya" nan da nan har
sunyi ciki dashi sun bace" tsofaffin 'yan sandan
biyu suka kalli juna cikin tsananin murna" sannan
suka fice da sauri domin su kaiwa kwamishina ya
bude ya basu nasu kason"
Cikin minti uku har sun garxaya a mota sun sami
DANMASANI" yana ta kai da kawowa a wani
kebantaccen gida na sirri da ya ce su sameshi
acan idan sun amso akwatin kudin"
Yana a tsaya yana kallonsu suka tunkareshi da
akwatin suna fara.a ganin haka saiya shiga cikin
wani daki na sirri" tsofaffin 'yan sandan suka
bishi" ciki suka sameshi har ya xauna akan kujera
ya dora hannuwanshi akan teburin dake a gaban
kujerar fara.a akan fuskarshi da kuma murnar
ganinsu"
.
.
"me kuka tsaya jira tun daxun ina xama jiranku?"
DAN MASANI" ya tambauesu yana shapa
bindigarshi dake a boye a kugunshi domin ya
tabbatar tana nan"
sai jangwarxo yace-:
"mun sami matsala ne a wurin nemanshi" domin
kuwa da farko tashar jirgin sama da kuma na
kasa muka tura yara su nemoshi" sai daga baya
muka sami cikakken bayanin an ganshi ya hau
wata mota ta haya da akwatin xai nufi wani
kauye ya boye acan" kafin yara subi motar yayi
nisa" amma an samu sa.a sunxo mana dashi
yana can gidan tuhuma munce su boyeshi sai
sunji daga garemu" Ga akwatin kudin munxo
dashi"
.
.
Suka ajiye akwatin a gaban kwamishina Dan
masani" sannan suka bushe a tsaye suna jiran
umarni daga wurinshi" da farko yaso nan take ya
ciro bindigar ya gama dasu" to amma kuma saiya
canxa shawara" ya kamata ya bude akwatin
domin ya dauke hankalinsu" idan suka mayar da
hankalinsu wajen kallon kudin sai ya harbesu a
tsanake"
.
.
DAN MASANI" ya ciro wani siririn mabudi a
aljihunshi ya saka a cikin kwadon akwatin ya
dade yana mirxawa" xuwa can sai kwadon ya
bude" kwamishina yayi murmushin farin ciki tun
kafin yasa hannu ya bude murfin yaga abinda
yake ciki" ya dubi 'yan sandan dake a tsaye a
gabanshi suna ta xufaa" yace dasu"
"to ina fatan dai kowa a cikinku ya gama tunanin
abubuwan da xaiyi da wadannan kudi" domin
kuwa da xarar mun kammala rabasu" xamuyi
ritaya" sai kowa ya nemi kwakkwaran kasuwanci
ya para" nidai dama na gama nawa tunanin kasar
ingila xan koma da xama" ban sani ba ko kuma
kun kammala taku shawarar"
.
.
A-C-P ßILYA yace dashi"
"mu dukanmu yallabai mun gama shirya inda
xamu nufa" samun kudin dama ai yafi sarrafasu
wahala"
suka tuntsire da dariya a lokaci guda"
kwamishina Danmasani yayi dariyar mugunta"
sannan ya bude murfin akwatin" manyan 'yan
sandan uku suka ja da baya a tsorace cikin
tsananin rudani" a yayin da suka ci karo da
abinda ke cunkushe a cikin akwatin" wasu jibgin
kaya ne an kimshesu suna ta faman tsami" da
kuma littafan karatu da takalma" a kusa da wani
kallabi wani katin shaida ne na jami.a wanda ke
dauke da hoton kyakkyawar budurwa tana ta
fara.a a gepen hoton an rubuta sunanta da
mayan bakake" #RALIYA_A_MUNTARI
.
=======>*****^*****<======
:
NAZIRU ya farfado daga suman tsayen" yayi sauri
ya rupe murfin akwatin domin kada wani yaxo
wucewa ya hango makudan kudin dake a ciki"
SHEGEN SAMA yayi ajiyar xuciya ya tambaya"
"A ina ka samo wannan akwatin naziru?" A ina ka
samo wadannan kudi haka...?"
Naziru ya daga kai ya dubeshi cikin tsananin
firgici yace dashi"
"Wallahi nima wurin RALIYA kanwata na amsoshi
ita ta bani da hannunta tace inxo in bude mata"
ina kyautata xaton ita kanta bata san abinda ke
cikin akwatin ba"
.
.
SHEGEN SAMA yayi murmushin farin ciki yace wa
Naziru"
"Allah ne ya bamu wannan makudan kudi Naziru"
domin kuwa babu wanda yasan daga ina suke"
Abinda yafi kawai shine mu rabasu ni da kai
kowa ya gudu yabar garin" muje can wata duniya
mu boye ba wanda zai sake jin labarinmu har
abada"
.
.
NAZIRU ya harareshi sannan yace-:
"Vaka da hankali SHEGEN SAMA" kana
tsammanin akwai rabonka a cikin wadannan
kudin?" to wannan kudi nawa ne ni da kanwata"
sai naga dama in dauko wani abu a ciki in dan
tsakura maka domin kuwa ka riga ka gani"
.
.
SHEGEN SAMA ya hade fuska yace da Naziru-:
"Kai ma kasan cewar wannan baxae taba yiwuwa
ba" dole ne mu raba wannan kudin mu biyu"
.
In ba haka ba daga nan.....
SHEGEN SAMA" ya hade fuska yace da Naziru"
"kai ma kasan cewar wannan bazai taba yiwuwa
ba" dole ne mu raba wannan kudin mu biyu" in ba
haka ba daga nan xan hau keke inje in sanarwa
'yan sanda acan gari suxo su amshi kudin da
hannunsu"
Naziru ya kurawa shegen sama idanu cikin
tsananin kulewa" ya dade da sanin halinshi na
rashin sabo" akan dan abu kankani zai iya yiwa
koda uwarshi rashin mutunci ne" kuma Naziru ya
tabbatar idan har bai yarda sun raba kudin ba" to
ko shakka babu shima yayi asararsu" domin
kuwa kai tsaye shegen sama xai wuce xuwa
wurin 'yan sanda"
.
.
NAZIRU yace dashi-:
"to naji xamu raba kudin" amma uku xamu raba
duk da kanwata RALIYA kowa ya dauki kaso dai-
dai"
SHEGEN SAMA ya sake murtuke fuskarshi" duk
yayi sharkaf da xupa kamar kuturu yace da
Naziru"
"Baxan taba amincewa ka ha'inceni ba Naziru"
domin kuwa ba yau ka fara yi min irin wannan
hadamar ba" kudi mu biyu muka tsince su ni da
kai" kuma mu biyu xamu rabasu" idan baka
amince ba" sai dai kowa ya hankura akaiwa 'yan
sanda su raba"
.
.
NAZIRU ya kidime yana durkushe ya dafa akwatin
kudin da hannunshi" hakika shegen sama ba
abokin amana bane" domin kuwa irin wannan ta
taba faruwa a tsakaninsu" a lokacin da suka
shiga gidan fulani dake a bayan gari suka sato
agwagi biyar suka xuba a cikin buhu" Naziru ya
barwa shegen sama agwagin kafin jama.a su tafi
gona su tafi dasu gari su sayar a kasuwa"
Lokacin da Naziru ya biyo ta gidansu shegen
sama" tuni har yakai gari ya sayar da agwagin"
haka sukayi ta rigima akan kudin har yanxu bai
gama biyanshi nashi kason ba"
Don haka a wannan karon Naziru yasan cewar
koda ace amincewa yayi su raba kudin biyu da
shegen sama" dole ne saiya ha'inceshi" saboda
tsabar hadama" don haka ya xama dole yayi
kokari yayi maganin shegen sama" a wannan
karon"
.
.
NAZIRU yace dashi-:
"Naji na amince xamu raba kudin mu biyu" to
amma baxae yiwu mu raba wadannan kudin
yanxu ba" saidai mu boye su xuwa nan da kwana
biyu idan babu wani abu da ya faru" saimu ciro
abinmu sun xama namu"
shegen sama ya xaro idanu cikin rashin yarda"
yace da Naziru"
"A ina xamu boye wadannan makudan kudi?"
Naziru yace-:
"muje can fadamarmu mana mu boye su" mu
gina rami mu binne akwatin bayan komai ya lafa
saimu tono abinmu mu raba"
.
.
SHEGEN SAMA" yayi shiru cikin xargi" xuwa can
yace"
"xan aminci muyi hakan" amma kai ma ka amince
idan muka binne wadannan kudin to baxan yarda
ka matsa daga inda nake ba" sai dai ka dawo
nan dakina mu rika kwana tare" ko bayi xaka
shiga sai dai mu shiga tare" domin nasan
ha.incinka NAZIRU so kake yi ka ha"inceni ban
yarda dakai ba"
Naziru yace dashi-:
"Na amince" xomu tafi bakin rafi mu binne
akwatin nan shegen sama" domin kuwa idan
tsautsayi ya ratsa sai kaga wani shegen ya karu
mun xama mu uku"
shekiyan samarin biyu suka fito daga cikin xauren
NAZIRU yana rungume da akwatin a hannunshi"
shegen sama yana binshi a baya" suna tafiya
xugum-xugum sai kace xauje jana.ida" bayan
sunje bakin fadamar ne" inda ke cunkushe da
shuke shuke" dangin kabewa da kuma tumatir"
wani bangaren kuma gonakin rake ne da kuma
kubewa 'yar damina"
Naziru ya nuna gindin wata bishiyar dorawa dake
a saman tudu kafin a gangara cikin fadamun a
nufi bakin rafi"
.
.
"A gindin bishiyar can ya kamata mu boye kudin
nan" ya cewa shegen sama yana nan cikin xargi
ko fara.a baya yi" ya girgixa kai bai cewa Naziru
komai ba" yana ta kaffa-kaffa dashi domin kada
ya tsere da akwatin yabar shi" xuwa can sai suka
samo magirbi a cikin fadamar tumatirin wadanda
masu aiki suke ajiyewa kafin su dawo washegari"
Naziru ya mikawa shegen sama daya ya ajiye
akwatin a gepe daya" shima ya dauki magirni
daya" nan da nan suka dara gina rami sam! Sam!!
Kamar suna gina kabari" bayan sunyi nisa da
aiki" ramin yayi fadi sai suka dawo suna haka
cikin ramin daya bayan daya" idan wanna ya gina
ya gaji" sai ya fito ya barka dayan shima ya
gina" a haka har suka kammala gina dogon
ramin"
Naziru ya dauki akwatin ya saka a ciki yabar shi
a tsaye" suka sa hannu suka tura kasar ta cike
ramin" sannu a hankali suka rufe saman akwatin
suka haye saman ramin suna tattakawa domin
wurin ya saje da sauran kasar fadamar"
.
.
Bayan sun kammala ne sai Naziru ya kwashe
magirban ya rike daya a kowanne hannunshi" ya
daga kanshi sama a tsorace ya cewa shegen
sama"
"waccan jirgin menene"
shegen sama" anya kuwa bamu suka biyo ba?"
Shegen sama ya daga kanshi a tsorace ya kalli
sama" yana kokarin ganin jirgin da Naziru ke
nuna mashi" ba xato da tsammani sai yaji wani
abu mai kama da guduma ya tsaga mashi kokon
kai tas!!
.
.
Shegen sama yayi kururuwa sannan ya xube a
kasa yana kokarin ya dafe kanshi ne" sai naziru
ya sake daga magirbin ya dankara mashi a kokon
kai" kan shegen sama ya sake tarwatsewa"
idanuwanshi suka kakkafe............
Created at 2018-02-17 06:01:05
Back to posts
UNDER MAINTENANCE